• About
  • Sitemap
  • Privacy and Policy
  • Facebook
  • Contact Us
ONLINE REPORTERS
  • Home
  • TUTORIALS
    • Blogging
    • Download
    • News
    • Others
  • Online Money
    • Social Media
    • Mobile Tips
  • Nokia tutorials
  • Free Browsing
  • Computer
  • Android
Home » Hausa » Amarya ta 'kashe' jaririn kishiyarta da tafasasshiyar miyar kubewa

Amarya ta 'kashe' jaririn kishiyarta da tafasasshiyar miyar kubewa

Bismillahi... 

Rundunar 'yan sandan jihar Jigawa a arewacin Najeriya ta ce tana tsare da wata amarya wadda ta watsa wa uwargidanta tare da danta dan wata 10 tafasasshiyar miyar kubewa a jikinsu.

Mai magana da yawun 'yan sandan jihar, CP Abdu Jinjiri ya shaida wa BBC cewa lamarin ya faru ne a garin Gantsa da ke karamar hukumar Buji ta jihar.
Sai dai ya ce jajririn ya mutu sanadiyyar abin da ya faru.
CP Jinjiri, ya ce akwai rashin jituwa a tsakanin kishiyoyin.
Amaryar wadda ba ta wuce shekara 20 da haihuwa ba tana dakin girki ne a lokacin da uwargidan, rungume da danta, ta shiga dakin dafa abincin, daga nan, sai amaryar ta fara mayar mata da magana.
Daga nan sai cacar baki ta kaure. Ba tare da ba ta lokaci ba ne kuma amaryar ta dauki tukunyar miya tana tafarfasa ta watsa wa uwargidan da danta a jikinsu.
Bayan ta watsa musu miyar ne amaryar kuma ta fara ihu tana neman a kawo musu dauki.
Mai magana da yawun yan sandan ya ce uwargidan tana babban asibitin Dutse tana karbar magani, kuma duk jikinta ya daye, amma yaron ya rasu.
Kwamshinan 'yan sandan jihar CP Bala ya bayar da umarnin a kai amaryar da ta aikata lamarin sashen binciken kwakwaf domin gudanar da bincike da kuma yi mata hukuncin da ya dace.
BBC ta yi kokokarin jin ta bakin mijin matan wato Malam Hamza, amma wayarsa a rufe.
Posted by Unknown on Thursday, 16 August 2018 - Rating: 4.5
Title : Amarya ta 'kashe' jaririn kishiyarta da tafasasshiyar miyar kubewa
Description : Bismillahi...  Rundunar 'yan sandan jihar Jigawa a arewacin Najeriya ta ce tana tsare da wata amarya wadda ta watsa wa uwargidanta t...

Share this post on

Facebook Google+ Twitter
Amarya ta 'kashe' jaririn kishiyarta da tafasasshiyar miyar kubewa
2018-08-16T11:22:00-07:00
Unknown
Hausa|
Newer Post
Older Post
Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Followers

SUBSCRIBE our Daily Posts for free

Enter your email address:

Delivered by FeedBurner

Auto Add

Labels

Android Blogging Computer Download Free Browsing Gossip Hausa Internet Islam Lifestyle Mobile Tips Music Must Read News Nokia tutorials Online Money Others Social Media sports

SEARCH ENGINE

SUBSCRIBE OUR DAILY UPDATES FREE

Subscribe our free daily updates

 Subscribe to Our RSS Feed
Get this widget Now

Google Translate

Popular Posts

  • Man Utd sack Mourinho after poor start to the season
    The Red Devils have won just two of their last eight matches in all competitions and sit 11 points off fourth place in the Premier League J...
  • Top 10 Richest Hausa Kannywood Actors And Actresses In Nigeria 2018
    Nigeria is a country known for it different ethnicity and tradition , one of the majority group is the Hausa. Nigeria Entertainment World is...
  • Takaidattun labaran ranar Laraba 5/12/2018
    Shugaba Buhari ya bayar da umurnin a hanzarta sayowa sojojin kasar nan makamai. A yau an shiga rana ta biyu da yajin aikin ma'aikatan m...
  • Get Etisalat 11GB at just 1700 Naira and valid for a month
    BISMILLAHI.. This is unbeliable. You can now enjoy etisalat 11GB data at just 1700 Naira bank payment or 1900 for recharge card  payment...
  • Bidiyon Yadda Buhari ya rera wakar Kirsimeti
    Shugaban Muhammadu Buhari ya taya kiristocin Najeriya murnar bikin kirsimeti ta hanyar rera waka. A wani hoton bidiyo da shugaban ya wallaf...
  • Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu
    Al’umma a kasar Afirka ta Kudu, musamman tuzurai da suka haura shekara 18 a duniya, amma ba su yi aure ba sun shiga rudani, bayan sun samu l...
  • Na san masu yi min fatan mutuwa — Buhari
    Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya ce mutane da dama sun yi masa fatan mutuwa a lokacin da yake jinya a 2017. Shugaban ya bayyana haka...
  • "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai
    "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai ------...
  • I have better things to do with my life than being a governor, says El-Rufai
    Governor of Kaduna State, Mallam Nasir El-rufai, said that he has better things to do with his life than being the governor of Kaduna State...
  • Buhari approves NYSC, Law School for NOUN graduates
    President Muhammadu Buhari has assented to the National Open University Amendment Act, to allow the institution to operate as all other univ...

GOOGLE INDEX


About Me

Unknown
View my complete profile
Copyright © 2016 ONLINE REPORTERS - All Rights Reserved
Design by MUJAHEED NASEER - Blogger Templates - Powered by Blogger