• About
  • Sitemap
  • Privacy and Policy
  • Facebook
  • Contact Us
ONLINE REPORTERS
  • Home
  • TUTORIALS
    • Blogging
    • Download
    • News
    • Others
  • Online Money
    • Social Media
    • Mobile Tips
  • Nokia tutorials
  • Free Browsing
  • Computer
  • Android
Home » Hausa » Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu

Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu

Al’umma a kasar Afirka ta Kudu, musamman tuzurai da suka haura shekara 18 a duniya, amma ba su yi aure ba sun shiga rudani, bayan sun samu labarin cewa za su fara biyan haraji saboda ba su da aure.

An nuna cewa, samarin yankin Nkuthu na Arewacin KwaZulu-Natal, za su rika biyan harajin da aka sa wa suna harajin ‘samari marasa aure’ inda duk saurayin da ya haura shekara 18 ba tare da ya yi aure ba, zai rika biya haraji duk shekara, kamar yadda kafar labarai ta News 24 ta ruwaito.
Tashar eNCA, ta zanta da wani saurayi mai suna Thamsanka Zwande mai shekara 31, wanda bai da aure, kuma yana zaune ne a kauyen Bulamehlo na yankin Nkuthun da aka sanya dokar, inda ya ce har yanzu bai da aikin yi, don haka sai dai mahaifiyarsa ta biya masa harajin.

A rahoton da News 24 da kalato daga eNCA, duk saurayin da ya haura shekara 18, an aika masa takardar fara biyan kudin haraji duk shekara.
Zwande ya nuna cewa, “Eh, lallai an aiko min da takardar. Ba ni da mace ko budurwa da take zama da ni. Don haka zan rika biyan Randi 50 duk shekara.”

Rahoton ya kara da cewa wannan haraji zai shafi iyaye, domin duk wanda yake da dan da ya kai biyan harajin amma bai da aikin yi da zai biya wa kansa, dole nauyin biyan ya koma kan iyayensa.

Wani mai suna Busisiwe Mthembu, wanda yake da ’ya’ya samari guda uku da za su rika biyan harajin, ya shaida wa eNCA cewa, “Dole za su biya wannan harajin duk da cewa ba su da aikin yi. Na biya wa dana na farko, yanzu sauran biyu ma za su kai shekara 18 kwanan nan, dole in karbo musu takardar harajin.

Da yake jawabi game da zargin tursasa mutane da biyan kudi, basaraken yankin da ake kira iNkosi a kabilar Zulu, Thathezakhe Ngobese ya musanta zargin, inda ya ce kawai suna karbar kudi ne domin su yi amfani da shi wajen kula da masarautar da ma’aikatanta, “Amma ba iyalan Ngobese ake tara wa kudin ba,” inji shi.

Ba a Afirka ta Kudu aka fara sanya irin wannan dokar ba, tarihi ya nuna cewa an taba sanya irin wannan dokar a birnin Rum a shekara ta 9 Miladiyyar Annabi Isa, inda basaraken lokacin mai suna Agustus ya sanya doka mai suna “Led Papia Poppaea” domin ya kwadaitar da matasa su yi aure.

Haka kuma a Jihar Missouri ta Amurka, an taba sanya dokar biyan harajin Dala Amurka 1 a kan duk saurayin da bai da aure.

Posted by Unknown on Thursday, 6 December 2018 - Rating: 4.5
Title : Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu
Description : Al’umma a kasar Afirka ta Kudu, musamman tuzurai da suka haura shekara 18 a duniya, amma ba su yi aure ba sun shiga rudani, bayan sun samu l...

Share this post on

Facebook Google+ Twitter
Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu
2018-12-06T02:56:00-08:00
Unknown
Hausa|
Newer Post
Older Post
Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Followers

SUBSCRIBE our Daily Posts for free

Enter your email address:

Delivered by FeedBurner

Auto Add

Labels

Android Blogging Computer Download Free Browsing Gossip Hausa Internet Islam Lifestyle Mobile Tips Music Must Read News Nokia tutorials Online Money Others Social Media sports

SEARCH ENGINE

SUBSCRIBE OUR DAILY UPDATES FREE

Subscribe our free daily updates

 Subscribe to Our RSS Feed
Get this widget Now

Google Translate

Popular Posts

  • Man Utd sack Mourinho after poor start to the season
    The Red Devils have won just two of their last eight matches in all competitions and sit 11 points off fourth place in the Premier League J...
  • I have better things to do with my life than being a governor, says El-Rufai
    Governor of Kaduna State, Mallam Nasir El-rufai, said that he has better things to do with his life than being the governor of Kaduna State...
  • Bidiyon Yadda Buhari ya rera wakar Kirsimeti
    Shugaban Muhammadu Buhari ya taya kiristocin Najeriya murnar bikin kirsimeti ta hanyar rera waka. A wani hoton bidiyo da shugaban ya wallaf...
  • What Cristiano Ronaldo did when Real Madrid stopped following him on social media amid airbrushing claims
    Cristiano Ronaldo completed a £100million transfer from Real Madrid to Juventus in the summer ending his nine-year tenure at the Bernabeu. ...
  • Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu
    Al’umma a kasar Afirka ta Kudu, musamman tuzurai da suka haura shekara 18 a duniya, amma ba su yi aure ba sun shiga rudani, bayan sun samu l...
  • Buhari approves NYSC, Law School for NOUN graduates
    President Muhammadu Buhari has assented to the National Open University Amendment Act, to allow the institution to operate as all other univ...
  • Top 10 Richest Hausa Kannywood Actors And Actresses In Nigeria 2018
    Nigeria is a country known for it different ethnicity and tradition , one of the majority group is the Hausa. Nigeria Entertainment World is...
  • El-Rufai drags ABU, KadPoly to court over N9.50bn unremitted taxes
    Kaduna State Government, through its Board of Internal Revenue, has taken two federal government institutions domiciled in the state, Ahmadu...
  • Na san masu yi min fatan mutuwa — Buhari
    Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya ce mutane da dama sun yi masa fatan mutuwa a lokacin da yake jinya a 2017. Shugaban ya bayyana haka...
  • "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai
    "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai ------...

GOOGLE INDEX


About Me

Unknown
View my complete profile
Copyright © 2016 ONLINE REPORTERS - All Rights Reserved
Design by MUJAHEED NASEER - Blogger Templates - Powered by Blogger