Shugaba Buhari ya bayar da umurnin a hanzarta sayowa sojojin kasar nan makamai.
A yau an shiga rana ta biyu da yajin aikin ma'aikatan majalisun kasa suka yi.
Mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ya nuna takaicinsa kan yadda wasu ke yi wa Buhari fatan mutuwa.
Kotu ta shaidawa Ibrahim Shekarau cewa dole sai ya yi bayanin kudaden makaman da ake tuhumarsa.
Archbishop din mabiyar darikar Katolika na Abuja, Cardinal Onaiyekan ya ce har yanzu babu wani sahihin dan takarar shugaban kasa a 2019.
Gwamnatin jahar Zamfara ta raba ma 'yan banga Babura 850 don yaki da 'yan bindiga.
Yajin aiki: An kasa cimma matsaya a tattaunawa tsakanin gwamnati da kungiyar Malama ASUU.
Kotu ta bai wa hukumomin tsaron Najeriya wa'addin kwanaki 3 su kamo tsohuwar ministan man fetur Diezani Allison Madueke daga Landan su gurfanar da ita gabanta.
Kamfanin NNPC ya ce babu wani kunci da al'ummar Najeriya za ta fuskanta a bana na man fetur.
Kasar Iran ta ce Amurka ba ta isa ta sanya mana takunkumi kan mai ba.
Shugaban Kasar Aljeriya Buteflika ya soke gana wa da Yariman Saudiyya bin Salman.
Wani rahoto da aka fitar ya sake bayyana irin zaluncin da ake kasar Myammar take yi wa Musulman Arakan.
EPL: Manchester City ta ci Watford 2:1 a wasan da suka buga jiya.
EPL: West Ham United ta ci Cardiff City 3:1 a wasan jiya.
Title : Takaidattun labaran ranar Laraba 5/12/2018
Description : Shugaba Buhari ya bayar da umurnin a hanzarta sayowa sojojin kasar nan makamai. A yau an shiga rana ta biyu da yajin aikin ma'aikatan m...