• About
  • Sitemap
  • Privacy and Policy
  • Facebook
  • Contact Us
ONLINE REPORTERS
  • Home
  • TUTORIALS
    • Blogging
    • Download
    • News
    • Others
  • Online Money
    • Social Media
    • Mobile Tips
  • Nokia tutorials
  • Free Browsing
  • Computer
  • Android
Home » Hausa » Yadda makwabcina ya yi wa 'yata fyade

Yadda makwabcina ya yi wa 'yata fyade

  • Akwai cikakkiyar zantawar da Fatima Zarah Umar ta yigame da matsalar fyaden, sai ku latsa alamar lasifika da ke sama don sauraro.
Ko wacce wayewar gari, sai an samu labarin aikata fyade a wani waje. Abin ya zama ruwan dare ta yadda fushinmu da babatunmu ba sa wani tasiri.
Abin har ya zama cewa mutane ba sa kaduwa sosai yanzu idan suka ji labarin fyade.
Idan kuwa abin ya shafi yara kanana ne, sai dai mu girgiza kai kawai mu ce Allah ya sauwake.
Muna tambayar kanmu ko me ya sa hakan? Muna tambayar kanmu dalilin da ya sa fyade ya zama ruwan dare a yanzu?
Muna tambayar ko me ya sa yaranmu ba su tsira ba yanzu ko da a cikin gidajenmu yayin da muka bar su da 'yan uwanmu?
Wa za a zarga? Shin hakan na nufin rashin mayar da hankalin iyaye kan sha'anin 'ya'yansu na sa a dinga cutar da yaran ta hayar lalata da su ba tare da sanin iyayen ba?
Na hadu da wata baiwar Allah mai suna Asabe a Kaduna. Wani makwabcinsu dan shekara 38 ne ya yi mata fyade. Mahaifiyarta ta gaya min cewa sun matukar amincewa da wannan mutum.
Ta sawa ranta cewa shi mutum ne mai son yara shi ya sa ba ta taba kawo komai a ranta ba. A takaice ma har a lokacin da ya fara cin zarafin 'yar tata ba ta zarge shi da komai ba, sai da wata makwabciyarta ta jawo hankalinta kan yada halayyar 'yar ke sauyawa da kuma irin jita-jitar da ake yadawa a unguwar.
Da na tambayeta ko ya aka yi ba ta lura ba, sai ta ce min hankalinta ya dauku wajen ganin ta wadata 'ya'yanta da abin da za su rayu na bangaren ci da sha da sutura.
Ina taya iyayen yaran da aka yi wa fyade jaje sosai. Da wahala kwarai mutum ya gane irin halin bakin cikin da suke samun kansu a ciki a yayin da suka gane cewa an zalunci 'ya'yansu.
Babban abin bakin cikin ma shi ne idan har wanda ya aikata hakan dan gida ne.
Me ya sa ake samun karuwar yi wa yara fyade? Hukumomi ne ba sa yin abin da ya dace don ganin an yi adalci?
Masu fyade nawa aka kai kotu aka kuma yanke musu hukunci?
Posted by Unknown on Sunday, 13 August 2017 - Rating: 4.5
Title : Yadda makwabcina ya yi wa 'yata fyade
Description : Akwai cikakkiyar zantawar da Fatima Zarah Umar ta yi game da matsalar fyaden , sai ku latsa alamar lasifika da ke sama don sauraro. K...

Share this post on

Facebook Google+ Twitter
Yadda makwabcina ya yi wa 'yata fyade
2017-08-13T03:55:00-07:00
Unknown
Hausa|
Newer Post
Older Post
Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Followers

SUBSCRIBE our Daily Posts for free

Enter your email address:

Delivered by FeedBurner

Auto Add

Labels

Android Blogging Computer Download Free Browsing Gossip Hausa Internet Islam Lifestyle Mobile Tips Music Must Read News Nokia tutorials Online Money Others Social Media sports

SEARCH ENGINE

SUBSCRIBE OUR DAILY UPDATES FREE

Subscribe our free daily updates

 Subscribe to Our RSS Feed
Get this widget Now

Google Translate

Popular Posts

  • Man Utd sack Mourinho after poor start to the season
    The Red Devils have won just two of their last eight matches in all competitions and sit 11 points off fourth place in the Premier League J...
  • Top 10 Richest Hausa Kannywood Actors And Actresses In Nigeria 2018
    Nigeria is a country known for it different ethnicity and tradition , one of the majority group is the Hausa. Nigeria Entertainment World is...
  • Takaidattun labaran ranar Laraba 5/12/2018
    Shugaba Buhari ya bayar da umurnin a hanzarta sayowa sojojin kasar nan makamai. A yau an shiga rana ta biyu da yajin aikin ma'aikatan m...
  • Get Etisalat 11GB at just 1700 Naira and valid for a month
    BISMILLAHI.. This is unbeliable. You can now enjoy etisalat 11GB data at just 1700 Naira bank payment or 1900 for recharge card  payment...
  • Bidiyon Yadda Buhari ya rera wakar Kirsimeti
    Shugaban Muhammadu Buhari ya taya kiristocin Najeriya murnar bikin kirsimeti ta hanyar rera waka. A wani hoton bidiyo da shugaban ya wallaf...
  • Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu
    Al’umma a kasar Afirka ta Kudu, musamman tuzurai da suka haura shekara 18 a duniya, amma ba su yi aure ba sun shiga rudani, bayan sun samu l...
  • Na san masu yi min fatan mutuwa — Buhari
    Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya ce mutane da dama sun yi masa fatan mutuwa a lokacin da yake jinya a 2017. Shugaban ya bayyana haka...
  • "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai
    "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai ------...
  • I have better things to do with my life than being a governor, says El-Rufai
    Governor of Kaduna State, Mallam Nasir El-rufai, said that he has better things to do with his life than being the governor of Kaduna State...
  • Buhari approves NYSC, Law School for NOUN graduates
    President Muhammadu Buhari has assented to the National Open University Amendment Act, to allow the institution to operate as all other univ...

GOOGLE INDEX


About Me

Unknown
View my complete profile
Copyright © 2016 ONLINE REPORTERS - All Rights Reserved
Design by MUJAHEED NASEER - Blogger Templates - Powered by Blogger