• About
  • Sitemap
  • Privacy and Policy
  • Facebook
  • Contact Us
ONLINE REPORTERS
  • Home
  • TUTORIALS
    • Blogging
    • Download
    • News
    • Others
  • Online Money
    • Social Media
    • Mobile Tips
  • Nokia tutorials
  • Free Browsing
  • Computer
  • Android
Home » Hausa » Atiku Abubakar: 'Zan binciki kowa idan na zama shugaban Najeriya'

Atiku Abubakar: 'Zan binciki kowa idan na zama shugaban Najeriya'

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya ce akwai dalilai da dama da suka sa shi neman shugabancin kasar a babban zaben 2019.
Ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da
Jimeh Saleh bayan wata ziyara da ya kai ofishin BBC da ke Landan a watan Afrilun bana - wato kafin tsayar da shi a matsayin dan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar PDP a zaben 2019.
A watan Disamabar bara ne Atiku Abubakar ya fice daga jam'iyya mai mulki ta APC, inda daga bisani ya koma jam'iyyar adawa ta PDP.
Fitaccen dan siyasar ya ce yana so ya tsaya takarar shugabancin kasar ne saboda ya gyara abubuwan da bai iya gyarawa ba, a tsawon shekara takwas da ya yi a matsayin mataimakin shugaban kasar.
"Ina neman shugabancin Najeriya saboda abubuwan da ban iya yi ba don ina mataimakin shugaban kasa, zan samu dama na yi su," in ji shi.
Ya ce zai fara ne da gyara tattalin arzikin kasar, idan ya samu nasarar zama shugaban kasar.
Atiku Abubakar ya ce yana da tabbacin 'yan kasar za su yi na'am da shi ta fuskar yaki da cin hanci da rashawa, inda ya ba da misali da yadda gwamnatinsu ta kafa hukumar EFCC.
Har ila yau ya ce babu wani da bai zai bincika ba idan ya samu nasarar zama shugaban kasa.
Sai dai ya musanta batun da wadansu suke yi cewa idonsa ya rufe wajen neman shugabancin Najeriya.
Hakazalika ya yi karin haske kan batun hana shi izinin shiga kasar Amurka, inda ya ce ya nemi bizar shiga kasar, "amma sun hana ni."
Sai dai da aka tambaye shi dalilin hana shi bizar ta shiga Amurka ya ce shi ma ba a gaya masa dalili ba.
Alhaji Attiku Abubakar ya kuma musanata cewa an yi gwanjon gidansa a Amurka, inda ya ce dama gidan matarsa ne da ya saya mata, kuma "ita ta sayar da kayanta," in ji shi.
Game da kalaman Shugaba Buhari kan matasa na baya-bayan nan, dan siyasar ya ce ra'ayinsa ya sha bamban da na shugaban, "ba na wa matasan kasar kallon cima zaune."
A karshe ya yi kira ga matasan kasar da su shiga harkokin siyasa, inda ya yi alkawarin ba su kaso 40 cikin 100 na ministocinsa idan ya samu nasarar lashe zabe.

Posted by Unknown on Saturday, 20 October 2018 - Rating: 4.5
Title : Atiku Abubakar: 'Zan binciki kowa idan na zama shugaban Najeriya'
Description : Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya ce akwai dalilai da dama da suka sa shi neman shugabancin kasar a babban zaben 2019. ...

Share this post on

Facebook Google+ Twitter
Atiku Abubakar: 'Zan binciki kowa idan na zama shugaban Najeriya'
2018-10-20T06:38:00-07:00
Unknown
Hausa|
Newer Post
Older Post
Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Followers

SUBSCRIBE our Daily Posts for free

Enter your email address:

Delivered by FeedBurner

Auto Add

Labels

Android Blogging Computer Download Free Browsing Gossip Hausa Internet Islam Lifestyle Mobile Tips Music Must Read News Nokia tutorials Online Money Others Social Media sports

SEARCH ENGINE

SUBSCRIBE OUR DAILY UPDATES FREE

Subscribe our free daily updates

 Subscribe to Our RSS Feed
Get this widget Now

Google Translate

Popular Posts

  • Man Utd sack Mourinho after poor start to the season
    The Red Devils have won just two of their last eight matches in all competitions and sit 11 points off fourth place in the Premier League J...
  • Top 10 Richest Hausa Kannywood Actors And Actresses In Nigeria 2018
    Nigeria is a country known for it different ethnicity and tradition , one of the majority group is the Hausa. Nigeria Entertainment World is...
  • Get Etisalat 11GB at just 1700 Naira and valid for a month
    BISMILLAHI.. This is unbeliable. You can now enjoy etisalat 11GB data at just 1700 Naira bank payment or 1900 for recharge card  payment...
  • Bidiyon Yadda Buhari ya rera wakar Kirsimeti
    Shugaban Muhammadu Buhari ya taya kiristocin Najeriya murnar bikin kirsimeti ta hanyar rera waka. A wani hoton bidiyo da shugaban ya wallaf...
  • Takaidattun labaran ranar Laraba 5/12/2018
    Shugaba Buhari ya bayar da umurnin a hanzarta sayowa sojojin kasar nan makamai. A yau an shiga rana ta biyu da yajin aikin ma'aikatan m...
  • Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu
    Al’umma a kasar Afirka ta Kudu, musamman tuzurai da suka haura shekara 18 a duniya, amma ba su yi aure ba sun shiga rudani, bayan sun samu l...
  • Na san masu yi min fatan mutuwa — Buhari
    Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya ce mutane da dama sun yi masa fatan mutuwa a lokacin da yake jinya a 2017. Shugaban ya bayyana haka...
  • "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai
    "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai ------...
  • I have better things to do with my life than being a governor, says El-Rufai
    Governor of Kaduna State, Mallam Nasir El-rufai, said that he has better things to do with his life than being the governor of Kaduna State...
  • Get 10GB Etisalat data at just 1500 and Valid for a month
    BISMILLAHI.. This is unbeliable. You can now enjoy etisalat 10GB data at just 1500 Naira for bank payment or 1800 for recharge card  pay...

GOOGLE INDEX


About Me

Unknown
View my complete profile
Copyright © 2016 ONLINE REPORTERS - All Rights Reserved
Design by MUJAHEED NASEER - Blogger Templates - Powered by Blogger