• About
  • Sitemap
  • Privacy and Policy
  • Facebook
  • Contact Us
ONLINE REPORTERS
  • Home
  • TUTORIALS
    • Blogging
    • Download
    • News
    • Others
  • Online Money
    • Social Media
    • Mobile Tips
  • Nokia tutorials
  • Free Browsing
  • Computer
  • Android
Home » Hausa » Ina 'yan sanda suka ajiye 'yan Shi'a 400 da suka kama?

Ina 'yan sanda suka ajiye 'yan Shi'a 400 da suka kama?

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce ta kama 'yan kungiyar 'yan Uwa Musulmi 400 da ake zargi da tayar da yamutsi a Abuja, babban birnin kasar.
Wata sanarwa da kakakin rundunar Mr Jomoh Moshood ya aike wa manema labarai ta kara da cewa an kama mutanen ne dauke da kwalabe 31 na bama-baman da aka hada da fetur da muggan makamai.
A cewar sanarwar ana gudanar da bincike kan 'yan Shi'ar kuma da zarar an kammala za a gurfanar da su a gaban kotu.
Mr Moshood ya zargi mabiyan Sheikh Ibrahim El-Zakzakky da kona motocin 'yan sanda da tayar da hargitsi inda ya ce babban sufeton 'yan sandan kasar ya ba da umarni ga 'yan sanda su murkushe 'ya'yan kungiyar a dukkan inda suke a fadin Najeriya.
"An sanya kwamishinonin 'yan sandan jihohin da akwai mabiya kungiyar 'yan Uwa Musulmi ta El-Zakzakky da su shiga cikin shirin ko-ta-kwana domin murkushe su kamar yarda doka ta tanada sannan su hana 'yan kungiyar tayar da kayar baya a jihohin," in ji sanarwar.
Tun daga karshen makon jiya ne dai mabiya El-Zakzakky suka soma isa Abuja inda za su yi gangami na jimanin mutuwar Hussain, jikan manzon Allah Annabi Muhammad(SAW) wanda ake yi duk shekara.
Sai dai sun yi zargin cewa jami'an tsaro sun hana su shiga lamarin da ya haddasa arangama tsakaninsu har aka yi asarar rayuka.
Wata sanarwa da rundunar sojin kasar ta fitar ranar Litinin ta ce an kashe mabiya Shi'a uku yayin da sojoji suka jikkata akamakon taho-mu-gamar da aka yi a tsakaninsu.
Sanarwar ta ce 'yan Shi'a sun far wa dakarunta da ke sanya ido a wuraren binciken ababen hawa da ke gadar Kugbo/Karu.
"Mabiya mazahabar wadanda ke da matukar yawa sun kutsa kai ta shingen binciken ababen hawa inda suka turmushe 'yan sanda.
"Daga nan ne 'yan sandan suka janye inda suka shiga cikin sojojin da ke yunkurin dakile harbe-harben da mutanen ke yi," in ji sanarwar.
Ta kara da cewa "lokacin arangamar ne mabiya mazahabar uku suka mutu san nan soji hudu suka jikkata, inda aka tura su asibiti domin karbar magani."
Amma 'yan Shi'a sun ce jami'an tsaron Najeriya sun kashe mambobinsu 24.
Masu sharhi sun shaida wa BBC cewa ya kamata gwamnati da mabiya mazhabar Shi'a su sasanta tsakaninsu domin gujewa abin da ka-je-ya-komo.

Posted by Unknown on Wednesday, 31 October 2018 - Rating: 4.5
Title : Ina 'yan sanda suka ajiye 'yan Shi'a 400 da suka kama?
Description : Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce ta kama 'yan kungiyar 'yan Uwa Musulmi 400 da ake zargi da tayar da yamutsi a Abuja, babban ...

Share this post on

Facebook Google+ Twitter
Ina 'yan sanda suka ajiye 'yan Shi'a 400 da suka kama?
2018-10-31T05:53:00-07:00
Unknown
Hausa|
Newer Post
Older Post
Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Followers

SUBSCRIBE our Daily Posts for free

Enter your email address:

Delivered by FeedBurner

Auto Add

Labels

Android Blogging Computer Download Free Browsing Gossip Hausa Internet Islam Lifestyle Mobile Tips Music Must Read News Nokia tutorials Online Money Others Social Media sports

SEARCH ENGINE

SUBSCRIBE OUR DAILY UPDATES FREE

Subscribe our free daily updates

 Subscribe to Our RSS Feed
Get this widget Now

Google Translate

Popular Posts

  • Man Utd sack Mourinho after poor start to the season
    The Red Devils have won just two of their last eight matches in all competitions and sit 11 points off fourth place in the Premier League J...
  • Top 10 Richest Hausa Kannywood Actors And Actresses In Nigeria 2018
    Nigeria is a country known for it different ethnicity and tradition , one of the majority group is the Hausa. Nigeria Entertainment World is...
  • Get Etisalat 11GB at just 1700 Naira and valid for a month
    BISMILLAHI.. This is unbeliable. You can now enjoy etisalat 11GB data at just 1700 Naira bank payment or 1900 for recharge card  payment...
  • Bidiyon Yadda Buhari ya rera wakar Kirsimeti
    Shugaban Muhammadu Buhari ya taya kiristocin Najeriya murnar bikin kirsimeti ta hanyar rera waka. A wani hoton bidiyo da shugaban ya wallaf...
  • Takaidattun labaran ranar Laraba 5/12/2018
    Shugaba Buhari ya bayar da umurnin a hanzarta sayowa sojojin kasar nan makamai. A yau an shiga rana ta biyu da yajin aikin ma'aikatan m...
  • Tuzurai za su rika biyan harajin rashin yin aure a Afirka ta Kudu
    Al’umma a kasar Afirka ta Kudu, musamman tuzurai da suka haura shekara 18 a duniya, amma ba su yi aure ba sun shiga rudani, bayan sun samu l...
  • "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai
    "Za mu wayar wa mutane kai kan zaben mutane nagari ba munafukai, barayi da wadanda ba su iya yi wa kan su aski" - El-Rufai ------...
  • I have better things to do with my life than being a governor, says El-Rufai
    Governor of Kaduna State, Mallam Nasir El-rufai, said that he has better things to do with his life than being the governor of Kaduna State...
  • Buhari approves NYSC, Law School for NOUN graduates
    President Muhammadu Buhari has assented to the National Open University Amendment Act, to allow the institution to operate as all other univ...
  • Get 10GB Etisalat data at just 1500 and Valid for a month
    BISMILLAHI.. This is unbeliable. You can now enjoy etisalat 10GB data at just 1500 Naira for bank payment or 1800 for recharge card  pay...

GOOGLE INDEX


About Me

Unknown
View my complete profile
Copyright © 2016 ONLINE REPORTERS - All Rights Reserved
Design by MUJAHEED NASEER - Blogger Templates - Powered by Blogger