Shugaba Buhari yana kokarin dinke barakar da ta shigo APC kafin 2019.
Shugaban kungiyar Izala, Bala Lau ya yaba ma Gwamna El-Rufa'i na Kaduna bisa daukan matakin gaggawa kan rikicin Kaduna.
Masu garkuwa da suka sace tagwayen nan a jihar Zamfara sun bukaci a biya su Naira milyan 150.
Wasu 'yanbindiga sun kai wani hari a kasuwan dabbobi da rana tsaka a jihar Taraba.
A jihar Neja za a yi wa mata 50 fida masu dauke da yoyon fitsari.
Sakamakon rikicin Kaduna an dakatar da safara da jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna.
A yau ne gwamnonin Najeriya za su yi taro don tattaunawa kan karin albashi don kaucewa yajin aikin kungiyar kwadago.
Tony Anenih, daya daga cikin wadanda su ka kyankyashi PDP ya mutu yana da shekaru 85.
Jamus ta goyi bayan matakan Turkiyya da Rasha akan Siriya.
An kai wata mummunar hari a Afghanistan har mutane biyar sun mutu.
Jirgin mai kungiyar kwallon kafar Leicester City ya yi hatsari.
EPL: Manchester United ta ci Everton 2:1 a wasan jiya.
LaLiga: Barcelona ta lallasa Real Madrid da ci 5:1 a wasan jiya.
Seria A: AC Milan ta ci Sampdoria 3:2 a wasan da suka buga jiya.
Title : Taqaitattun Labaran Safiyar Litinin 29/10/2018
Description : Shugaba Buhari yana kokarin dinke barakar da ta shigo APC kafin 2019. Shugaban kungiyar Izala, Bala Lau ya yaba ma Gwamna El-Rufa'i na ...