Abubuwa guda goma wanda ya aikata daya daga cikinsu, Allah zai gina masa gida a Aljanna:
Akwai wadansu aiyuka manya guda goma da Annabi s.a.w ya kwadaitar da al'ummarsa su aikata kuma har yace wanda ya aikata daya daga cikinsu Allah zai gina masa gida a Aljanna.
*1-Gina Masallaci*
(Masallaci ko islamiyya ko wata center ta Yada addinin musulunci).
@Bukhari da Muslim
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ 6128
*2-Karanta Suratul Ikhlasy sau 10*
(karanta Suratul Qul huwallahu Ahad sau goma da kyakkyawan karaatu).
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ 6472
@ﺍﻟﺴﻠﺴﻠﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ 2/126
3-Fadar *ALHAMDULILLAH da INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN* alokacinn da masifa ko wani bala'i ya sameka.
@ﺭﻳﺎﺽ ﺍﻟﺼﺎﻟﺤﻴﻦ 1 / 362
*4-Addu'a lokacin shiga kasuwa*.
(wanda ya karanta wannan addu'a lokacin shiga kasuwa yana samun abubuwa guda hudu:
*-Rubuta masa lada Miliyan guda-1,000,000*
*-Kankare masa Zunubai Miliyan guda 1,000,000*
*-Daukaka darajarsa sau Miliyan guda. 1,000,000*
*-Kuma za'a gina masa gida a aljanna)*.
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ ( 1/1118
Ga Addu'ar:
*"ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ﻟﻪ ﺍﻟﻤﻠﻚ ﻭ ﻟﻪ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻳﺤﻴﻲ ﻭ ﻳﻤﻴﺖ ﻭ ﻫﻮ ﺣﻲ ﻻ ﻳﻤﻮﺕ ﺑﻴﺪﻩ ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻭ ﻫﻮ ﻋﻠﻰ ﻛﻞ ﺷﻲﺀ ﻗﺪﻳﺮ"*.
*5-Cike gurbi a cikin Sahun Sallah*
(wanda ya ga wani gurbi aciki sahu sai yashiga da ya cike gurbin Allah zai gina masa gida a aljanna).
@ﺍﻟﺴﻠﺴﻠﺔ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ 4/515
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ 1843
*6-Kiyaye Sallolin Nafila Ratibai na dare da yini na Annabi s.a.w*
(wanda ya kikayaye salloli guda goma sha biyu a cikin dare da yini Allah zai gina masa gida aljanna).
@Muslim
@ﻭﺻﺤﻴﺢ ﺳﻨﻦ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﺑﻦ ﻣﺎﺟﺔ
*7-Wanda yayi imani na gaskiya ga Annabi s.a.w*.
(wanda yayi imani da Annabi s.a.w ya kuma yi hijira ko kuma yayi jihadi tare da shi ko yayi kokarin Yada sunnarsa bayan mutuwarsa Annabi s.a.w ya tsaye masa gida acikin aljanna).
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ [ 1 /
235
*8-Barin Jayayya da gardama koda kine kake da gaskiya*
(wanda yabar gardama ko tawasace ko shi yake da gaskiya amma yabar wannan gardama ko jayayya. Annabi s.a.w yacce ya tsaye masa gida a aljanna).
@ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ [ 3 /6
*9-Barin Karya koda ta wasace*.
(wanda ya kiyaye kansa daga karya koda karyace ta wasa Manzon Allah s.a.w. Ya tsaye masa gida a aljanna).
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ [ 3 / 6
*10-Wanda yake da kyawawan halaye da Dhabi'u*.
(wanda yake da dhabi'u da hali mai kyau Annabi s.a.w ya tsaye masa gida a madaukakiyar aljanna).
@ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ [ 3/6
Wanda Allah ya gina masa gida a aljanna, sai Annabi s.a.w ya koya mana aiyukan da zamuyi don mu kara kyautata wannan gida na aljanna da kayan itatuwa da kayan marmaari.
Fadar wannan zikiri:
ﺳﺒﺤﺎﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﻭﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﻠﻪ ﺃﻛﺒﺮ
Yana sanya Allah ya dasa maka itaciyoyi a cikin gidanka na aljanna.
@ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ 3460
Allah ne mafi sani.
Title : MUTANE GUDA GOMA ALLAH ZAI GINA MASU GIDA A ALJANNA
Description : Abubuwa guda goma wanda ya aikata daya daga cikinsu, Allah zai gina masa gida a Aljanna: Akwai wadansu aiyuka manya guda goma da Annabi s.a...